Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 11

Sponsored Links

BOOK 1đź“•

Free page 11 🦋

Karfe 9:10 na dare jirginsu ya sauka a murtala muhammad international Airport (MMIA) dake Garin lagos, wasu dankara dan karan motocine sukazo daukarsu,da kyar tahee take daga kafarta jin yadda kanta ke sara mata, mintuna 35 ne suka kaisu AL_NAHYAN EATATE dake banana island ,tundaga kan Layin gidan kan tahee ke matukar sarawa ga wani irin tsananin bugu da zuciyarta kema ta,ko ina da yalwataccen haske kamar ba dare ba , ta ko ina sojojine ke Sara musu, sosai tahee ta  rike hannun hijabinta gagam ganin irin sojojin dake gidan , sabida ydda zuciyarta ke bugawa sosai ta kulle idanuwanta , direct motocin part din hajiya kilishi suka nufa,sau biyu hajiya kilishi na kiran tahee amma bata masa ba , ana ukunne ta tabata sosai tahee ta ware idanuwanta, kallan ta hajiya kilishi tayi na yan sakanni kafun ta soma magana “ lapiyan ki kuwa “ gyada mata kai taheera tayi sai kuma ta bude bakinta” Kai na ne ke dan ciwo aunty “, cikin damuwa hajiya kilishi ta kamo hannunta ta futo da ita daga cikin motar”sannu kinji, nasan gajiya ce muje ciki kisha magani sai ki kwanta”nan ma gyada kanta tahee tayi batare da cewa komai ba,kafarta ta taka da soma tayifa sosai wani azababban zafi ke ratsa kafarta , kamar wacce ta dora kafarta a garwashi, ko wacce addua tazo bakinta yi take , nan da nan taji zafin ya tafi, haka suka karasa ciki tana bun hajiya kilishi a baya, dakin dake gefen star case ammi ta bude , “Bismillah tahee”, shiga ciki tahee tayi bakin dauke da Bismillah kamar ydda hajiya kilishi ta umarceta,”ga ban daki nan , zansa a kawo miki abinci da magani sai kishi ki kwanta”cewar hajiya kilishi,”na gode sosai aunty ,Allah ya saka da Alkairi”bata bari ta karasa ba ta katseta”Godiyar ta isa haka kisa mu ki huta”tana gama fadar haka ta bar dakin.itama toilet ta nufa tare da kama ruwa sannan tayo Alwala , tana fitowa ta tarar da jakar kayanta, hijab ta dauka tare da nufar inda dadduma take shinfide,sallolin da ake binta ta rama tana cikin addua ne aka kwankwasa kofar, Tashi tayi tare da budewa , wata budurwace ta shigo sanye da blue din Riga da dark blue din skeat ,”good day ma”cewar ta, murmushi kawai tahee tayi batare da ta amsa ba, abincin dake hannunta ta ajiye cikin center table din dake kusa da ita , cikin gurbatacciyar hausarta tace” madam tace na kawo miki abinci sannan kisha magani ki kwanta,”toh na gode”, jinjina mata kai budurwar tayi tare da furo mata kofa , abincin da aka kawo mata ta bude lafiyayyan abincine me rai da lapiya a ciki,sai kunun aya da aka sa mata cikin wani mini glass jug, daga gefen tray din wasu Kayan mar marine aciki, kadan ta tsakuri abincin “da oumma da taheer sunanan tare za muci abincin , nasan yanxu Suna can su kadai”, cewar tahee harta kammala cin abincin, kuskure bakinta tayi tare da watsa ruwa , sannan ta hau kan lapiyayyan gadon dakin ,lilliba tayi jin sanyi na ratsata ta ko ina , bata dade da kwanciya ba bacci ya dauke ta .

âž°âž°âž°âž°
A gajiye ya dawo gidan bayan zaki ya ajjesa, ko part din ammi be Jeba, Wanka kawai yayi tare da nufar down stairs , Kai tsaye kitchen din dake falon ya nufa, banban kitchen ne da ya gaji da haduwa komai na anfanin kitchen akwai shi a ciki,kitchen din sai faman daukan kyalli yake, coffee ya hada cikin coffee maker din kitchen din, kan daya daga cikin kujerun dining din kitchen din ya zauna, a hankali yake sipping coffee din dake hannunsa,bayan ya shanyene ya kara hada wani tare da barin kitchen din, stair case ya dau tare da nufar kofar hagunsa, taku kadan ya kai shi wasu kofofi guda uku, kofar tsakiya ya shiga , ya dau dogon lokaci a ciki kafun ya fito, stair case din da zai kaishi second floor ya hau, a hankali yake taka stairs din har ya karasa hawa saman, kan daya daga cikin kujerun falon ya zauna tare da fara operating din system dinsa, ya dade yana anfani da ita kafun ya kashe ta gaba daya , toilet ya nufa be dade ba ya fito tare da nufar faffadan gadonshi, remotes din fitulun part din ya kashe kafun ya kwanta cikin lallausan gadonsa, be dade da kwanciya ba bacci ya daukesa.

Wutace sosai take ci, da anzuba mata ruwa Sai ta kara tashi kamar wacce ake hurata , ga hayaki da ya gauraye ko ina, daga cikin wutar kuwa hannu ake miko masa cikin azaba “Akhee habeeby!!Akhee habeeby!!”hannunsa ya Mika da niyar ya kamo Wanda yake cikin wutar… farkawa king yayi sai faman hada gumi yake bayan sanyin Acn da ya cika dakin, adduoi ya fara karantawa a hankali wata nutsuwa tazo masa ,wayarsa dake side din gadan sa ya kunna,4:30shine abunda agogon ya nuna masa, mikewa yayi tare da nufar toilet, wanka ya fara yi kafun yayo Alwala, ya dade yana nafila kafun ai kirin sallah, direct kasa ya nufa bayan ya idar da sallahn , sanye yake cikin white jallabiya , sosai farar jallabiyar tayiwa surar jikinsa kyau,gashin kansa sanye yke cikin bakin rawanin larabawa, sosai kyawun fuskarsa ya fito, musamman idanuwansa da suka kara haske sai kyalli suke duk da kasancewar fuskarsa a hade yake,a hanyar zuwa Masallaci suka hadu da abeey shima zasu tafi masallacin,a haka motocin su suk fita , a dawo wa ma tare suka dawo gidan,Kai tsaye part din dada suka nufa dukansu, ganin babu kowa a falon yasa su samun waje ko wannan su ya zauna. Mintuna kadan sai gashi ta fita sanye da hijabi a jikinta , ko wannansu gaishe da ita yayi , yayinda take amsawa fuskarta washe da fara’a, kankance ido king yayi” dada yau naga sai fara a kike ko an miki albishir da zuwa umarace”a hankali yayi maganar amma duk da haka sai da ta jisa, hararar sa dada tayi”A’ah gorin daurin aurenka aka kawomun”kara hade fuska king yayi tare da dauke idanuwansa daga kanta,tabule baki dada tayi “Kai dai Kasani mutum kullum cikin daure fuska ,kamar audiga ina dalili”, be tanka mata ba sai ma lumshe ida nuwansa da yayi, abeey kam murmushi kawai yayi, hira suka dada ta fara tare da su uncle musaddiq , abeey na sa musu baki lokaci zuwa lokaci na yana kallan king, ganin hirar tasu bame karewa bace yayi musu sallama tare da nufar part dinsa. Gym room dinsa ya nufa , tare da sa kayn motsa jiki , ya dade  yana motsa jiki kafun ya futo duk ya hada zufa ,kwantaccen gashin kansa ya zubo masa har wajan idanuwansa,Wanka yayi tare da shirya cikin wani hadadden suit red colour, daddadan kamshin turaransa ya cika ko ina , gashin kansa ya sha gyada yayin da gefe guda na fuskar sa gashin ya futo harwajan idanuwansa,pink lips dinsa ya turo sosai , yayinda fuskarsa take a daure,sosai yayi kyau cikin shigarsa , sai ta kara futo da ainahin kalarsa ta larabawa,cikin takun sa ya bar part din , direct part din ummey ya nufa, har lokacin zoya bacci take , be dad’e ba ya bar part din tare da nufar part din ammi.

Yana shiga falan ya tarar da ba kowa a ciki sai yan aikin dake gyara dinning , suna ganinsa ko wanne jikinsa ya dau rawa, cikin rawar murya suka gaishe shi,da hannu kawai yayi musu alama , suna ganin haka sukai saurin barin wajan, kan daya daga cikin 2 sitter din kujerun ya zauna tare da crossing legs dinsa. Cikin shigar material ammi ta fito daga kitchen , hannunta dauke da tray din abinci, cikin na tsuwarsa ya mike tare da nufar inda take da nufin sauke mata tray din, girgiza masa kai tayi “no son,abincin daughter ne”, kallan ta yayi na yan sakanni kafun ya bude bakinsa” me ya kawo su part dinnan da sassafe”,hararar sa ammi tayi “Kai me ya kawo ka da sassafe, Kai tsaye ya bata amsa “to see my happiness “murmushi ammi ta sakar masa tana kara jin kaunarsa a ranta ,”ba abincin su amrah bane, wannan na sister dinka ce , you will see her soon”bai ce mata komai ba sai lumshe mata ido da yayi, itama Kai tsaye dakin da tahee take ciki ta nufa, akan dadduma ta tarar da ita , mikewa tayi tare da karban tray din hannun Amin ta ajje mata a gefe” ina kwana aunty”kallanta sosai Ammon tayi “from today ki kirani da ammi not aunty” jinjina mata kai tahee tayi sai kuma ta bude baki”insha Allah ammi” dariyar jin dadi ammi tayi “kin tashi lapiya, hope ciwan kan ya sauka”, “eh ya dena ammi”cewar tahee, “toh Allah ya kara sauki, ga breakfast nan in kin gama sai ki fito falo karkiyi ta zama a daki ke kadai”, jin jina mata kai tahee tayi “toh ammi na gode “, fita ammi tayi daga cikin dakin, TAHEE kuma waje ta Samu ta zauna “ya Allahu har na fara kewar ku oumma na da taheer dina “.
A falo kuwa har yanxu king na zaune ya lumshe idanuwansa “if not for ammi, who dare to keep him waiting”,lips dinsa na kasa ya fara tsotsa kwata kwata bazaka gane yanayinsaba, shafa gefan fuskarsa da akaine yasashi bude idanuwansa,ammi ya tarar a tsaye sai faman murmushi take saki, dauke kansa yayi daga kallanta,”sorry my son”, dago da idanuwansa yayi tare da kallanta “it’s okay , ammi am hungry “,am coming” kawai tace tare da komawa kitchen , hadadden breakfast dinsa da tayi masa shida tahee takawo masa , tsabar sarauta a baki take bashi,kadan yaci tare da Shan kunun ayan da yake matukar kauna,bayan ya kammala cin abincinsa ammi ta kallesa “son Yaushe zaka dawo gida”Kai tsaye ya bata amsa” it can be possible da yamma , kina bukatar wani abune “girgiza masa kai tayi “no son na tanbaya ne kawai”,mikewa yayi tare da pecking din goshinta “am going now”, take care shine abunda ammi tace masa , jinjina mata kai yayi tare da barin part din.

A daki Kuwa tahee wanka tayi bayan ta kammala cin abincin da ammi ta kawo mata, hijab dinta ta saka tare da kwashe kwanukan ta fito falo, Daidai lokacin da yan matan gidan ke shigowa, kallan tara saura kwata amrah ta bita dashi”ke kuma daga ina”,murmushin yake tahee ta saki”ina kwananku “wani hararan amrah ta bita dashi “bashi na tanbayeki ba”.ihsan ce ta katse mata zancen ta” easy amrah , ki bita a hankali mana”, kallanta ihsan tayi cikin sake fuska”yan mata ya sunan ki”, amsa mata tayi da “TAHEERA “tana sun kuyar dakai, lokaci d’aya zuciyar firdausi da amrah ya buga, “wow gaskiya kina da suna me dadi gaki kyakkyawa”,Shigowar ammi ne ya katse ihsan, “ah ah yan matana yana ganku a tsaye “, sumayyace tai saurin bata amsa “bakomai ammi mun shigone sai mukaga bakuwarki shine muke dan gaisawa”murmushi ammi tayi “kun kyauta kuwa , ku samu waje ku zazzauna , Kema tahee zo ki zauna”, kallan ammi tahee tayi “dama ina san wanke wadan nan kayan ne”girgiza mata kai ammi tayi “basai kin wahalar da kankiba”, wani dan button ta danna sai ga yan aiki guda biyu sun fito, kallan daya daga cikinsu ammi tayi “asabe ga kwanukwanan a hannun tahee su zaki kai kitchen”, toh hajiya cewar wadda aka kira da asabe,kwanukan hannun tahee asabe ta karba “nagode “murmushi asabe ta sakar mata ,”oya zo ki zauna “cewar ammi, waje ta samu daga kasa zata zauna ammi ta dakatar da ita, “ga waje zauna akan kujera”,batai musu ba ta hau daya daga cikin kujerun, “toh yan matana wannan sunan ta taheera ana ce mata tahee, Kema tahee wadaddan yayyunkine, wannan ta farkon ta nuna sumayya, sunanta sumayya,sai ihsan a kusa da ita , sai amrah da kuma firdausi”yawu firdausi ta hadiye”ammi ko itace wacce Kikace zaki kawo mana “, gyada mata kai ammi tayi, “tahee zata cigaba da zama tare damu, Inaso ku zauna kamar yadda nasan ku, hope zaku karbeta”, murmushin yake amrah ta saki “insha Allahu ammi”a haka suka dan taba hira kuwa da abunda yake sa’kawa a ransa, TAHEE ma duk a takure take ganin irin kallan da amrah take binta dashi,dama dama ihsan da ke janta da hira, sumayya da firdausi ko kallanta basa yi.

Zuciyarta tafarfasa take ba abunda take nanatawa sai “bazai yuba, it’s impossible “ tare da mikewa …..

Comment and share đź’–
Alkalamin Mss Lee ✍️

đź’–THE TALENT TROUPE WRITERS đź’–

LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA

             👇👇👇👇👇
DUK KARFIN IZZATA (star lady )

GIDAN AUNTY ( mss Lee)

JINI DAYA ( mrs bbk)

YA FITA ZAKKA( maman sayyid )

SARKI SAMEER( xeenat love)

Alkalamin Mss LEE✍️✍️✍️✍️
Ina Godiya masu commenting , I heart you allđź’–đź’–.

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA

đź’–đź’–GIDAN AUNTYđź’–đź’–
(A heart touching love story)

Story & written
By
Mss Lee đź’–

PAID BOOK
MAISAN COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button